Tinubu Ya Lashe Zaɓen Shugaban Najeriya Na 2023


Daga BBC Hausa 

Zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasar Naijeriya, Bola Ahmed Tinubu 

Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ya sanar da tsohon gwamnan jihar Legas, Bola Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa na 2023 da kuri’a miliyan 8,794,726.

Tsohon matainmakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ne ke biye masa da kuri’u miliyan 6,984,520.

Sai kuma dan takarar jam’iyyar Labour, Peter Obi wanda ya samu kuri’a miliyan 6,101,533.

Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ne ya zo na hudu da kuri’u miliyan 1,496,687.
Idan an jima ne kuma mutumin da ya yi nasarar wato Bola Ahmed Tinubu zai je dakin taron da ake tattara sakamako domin karbar shaidar lashe zaben.

Kusan za a iya cewa wannan ne sakamakon zaben da ya fi kowanne daukar dogon lokacin kafin a sanar da shi a baya-bayan nan sakamakon dalilai da dama.

Jam’iyyun adawa na PDP da LP sun ce ba za su karbi sakamakon ba bisa zargin tafka magudi a mazabu da dama, inda kuma suka ce za su garzaya kotu.

Ahmed Abdulkadir

Ahmed Tijjani Abdulkadir is a seasoned media executive, journalist, teacher, entrepreneur, and public servant with over 35 years of distinguished experience in broadcasting, media regulation, public communication, and education. He currently serves as the Chairman of the Katsina State Radio and Television Service Board and holds several leadership positions in the private sector. He is the Chairman of Namowa MediaHub and Barau & Namowa Agro-Allied and General Services, as well as the Managing Director of Broadsphere Ventures Limited and Managing Director of FASAB Foods Nigeria Ltd. Mr. Abdulkadir holds a Master’s degree in Development Studies from Bayero University, Kano, and a Bachelor of Education (Language Arts) from Ahmadu Bello University, Zaria. He also possesses professional qualifications in journalism and broadcasting from the International Institute of Journalism (IIJ) Abuja, NTA Television College Jos, and The Thomson Foundation/British Council, and a Certificate in Digital Journalism (Reuters/Meta Journalism Project).

Post a Comment

Previous Post Next Post