Gwamna Masari da Magoya bayan APC Sun Yi Zagayen Murnar Nasarar Tinubu

Daga Gwagware Media Reporters 

A ranar Laraba 1/03/20223, dubban ƴan jam'iyyar APC su ka fito kan tituna suna taya zaɓaɓɓen shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu murna.


Shi ma mataimakin dan takarar gwamnan jihar Katsina a karkashin jam’iyyar APC, Hon. Faruq Lawal Joɓe, ya na cikin jerin gwanon da su ka bi ta manyan tituna, daga bisani kuma su ka yi dandazo a dandalin jama’a (people's square) na gidan gwamnati.

Da ya ke jawabi ga magoya bayansa, Gwamna Aminu Bello Masari ya ce Katsina ta yi iya bakin ƙoƙarinta wajen ganin ta mara wa APC baya kuma in Allah Ya yarda za mu samu nasara a zaɓe mai zuwa.

“Mun yi imanin cewa Katsina za ta ci gaba a karkashin Dikko Radda da kuma Naijeriya a ƙarƙashin Ahmed Bola Tinubu, zaɓaɓɓen shugaban ƙasa.

“Mu godewa Allah da ya yi biyayya ga gwamnatin APC bisa la’akari da irin wahalhalun da mutane ke ciki musamman canjin kuɗaɗe, taɓarɓarewar naira da ƙarancin man fetur amma duk da haka, ta yi nasara a zaɓen shugaban ƙasa da ya haɗa da ƴan takarar majalisar wakilai tara, da dukkan kujerun sanatoci 3 a jihar.

“A zaɓen watan Maris, Insha Allahu, duk ƴan takarar APC za su lashe kujerunsu ba tare da tangarɗa ba, domin Dikko ne kaɗai ɗan takara da mu ke da shi wanda zai iya tuƙin jihar.”

Ahmed Abdulkadir

Ahmed Tijjani Abdulkadir is a seasoned media executive, journalist, teacher, entrepreneur, and public servant with over 35 years of distinguished experience in broadcasting, media regulation, public communication, and education. He currently serves as the Chairman of the Katsina State Radio and Television Service Board and holds several leadership positions in the private sector. He is the Chairman of Namowa MediaHub and Barau & Namowa Agro-Allied and General Services, as well as the Managing Director of Broadsphere Ventures Limited and Managing Director of FASAB Foods Nigeria Ltd. Mr. Abdulkadir holds a Master’s degree in Development Studies from Bayero University, Kano, and a Bachelor of Education (Language Arts) from Ahmadu Bello University, Zaria. He also possesses professional qualifications in journalism and broadcasting from the International Institute of Journalism (IIJ) Abuja, NTA Television College Jos, and The Thomson Foundation/British Council, and a Certificate in Digital Journalism (Reuters/Meta Journalism Project).

Post a Comment

Previous Post Next Post