Sabon Angon Naijeriya Ya Ziyarci Jihar Katsina

Daga Katsina Gazette 

Ƙasa da awanni 24 da ayyana shi a matsayin zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Naijeriya, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya sauka birnin Katsina a ranar Laraba.

Sabon angon Naijeriyar, Bola Tinubu, ya sauka a jihar ta Katsina ne, bayan an ayyana shi a matsayin zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Naijeriya a cikin daren ranar Talata, inda ya sauka a filin sauka da tashin jiragen saman jihar ta Katsina.

A yayin saukarsa, Tinubu, ya sami tarbar gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari, da mataimakinsa Alhaji Mannir Yakubu.


Tinubu da tawagarsa sun shigo Katsina, daga bisani su ka wuce Daura don ganawa da shugaban ƙasa Buhari da ke hutun zaɓe yanzun haka a gidansa da ke Daura.

Ahmed Abdulkadir

Ahmed Tijjani Abdulkadir is a seasoned media executive, journalist, teacher, entrepreneur, and public servant with over 35 years of distinguished experience in broadcasting, media regulation, public communication, and education. He currently serves as the Chairman of the Katsina State Radio and Television Service Board and holds several leadership positions in the private sector. He is the Chairman of Namowa MediaHub and Barau & Namowa Agro-Allied and General Services, as well as the Managing Director of Broadsphere Ventures Limited and Managing Director of FASAB Foods Nigeria Ltd. Mr. Abdulkadir holds a Master’s degree in Development Studies from Bayero University, Kano, and a Bachelor of Education (Language Arts) from Ahmadu Bello University, Zaria. He also possesses professional qualifications in journalism and broadcasting from the International Institute of Journalism (IIJ) Abuja, NTA Television College Jos, and The Thomson Foundation/British Council, and a Certificate in Digital Journalism (Reuters/Meta Journalism Project).

Post a Comment

Previous Post Next Post