Ƴan Takarar Gwamna A Jihar Katsina Sun Sa Hannu Kan Yarjejeniyar Zaman Lafiya.

Daga Gwagware Media Reporters 

Ƴan takarar gwamna na jihar Katsina da za su fafata a zaɓen 2023 sun sanya hannu kan shirin zaman lafiya na 2023 wanda hukumar zaɓe ta ƙasa mai zaman kan ta, wato (INEC) reshen jihar Katsina ta shirya, a babban ɗakin taro na ƴansanda da ke titin Kangiwa, GRA, Katsina, ranar Litinin, 20 ga watan Fabrairu 2023.

Ɗan takarar gwamnan jihar Katsina karkashin tutar jam'iyyar APC, Dakta Dikko Umaru Radda, ya na ɗaya daga cikin ƴan takarar da su ka samu halartar taron.


 A lokacin da ya ke zantawa da manema labarai ya shaida ma su cewa, wannan yarjejeniya za ta karfafa damokaraɗiyya a jihar Katsina. Sannan, ya tabbatar da bada cikakken haɗin kai don ganin an yi zaɓe cikin kwanciyar hankali da lumana. Kuma, ya bayyana cewa zai karɓi sakamakon zaɓe ko wane iri muddin an yi shi a cikin inganci da sahihanci. 

Shugaban hukumar fararen kaya, wato, DSS, ya gode ma ƴan takarar gwamna, shugabannin jam'iyyu, iyayen ƙasa da kuma jami'an tsaro yadda su ka nuna haɗin kai da goyon baya don ganin an gudanar da zaɓe cikin zaman lafiya.

Ahmed Abdulkadir

Ahmed Tijjani Abdulkadir is a seasoned media executive, journalist, teacher, entrepreneur, and public servant with over 35 years of distinguished experience in broadcasting, media regulation, public communication, and education. He currently serves as the Chairman of the Katsina State Radio and Television Service Board and holds several leadership positions in the private sector. He is the Chairman of Namowa MediaHub and Barau & Namowa Agro-Allied and General Services, as well as the Managing Director of Broadsphere Ventures Limited and Managing Director of FASAB Foods Nigeria Ltd. Mr. Abdulkadir holds a Master’s degree in Development Studies from Bayero University, Kano, and a Bachelor of Education (Language Arts) from Ahmadu Bello University, Zaria. He also possesses professional qualifications in journalism and broadcasting from the International Institute of Journalism (IIJ) Abuja, NTA Television College Jos, and The Thomson Foundation/British Council, and a Certificate in Digital Journalism (Reuters/Meta Journalism Project).

Post a Comment

Previous Post Next Post